Muna da Hadin Kai
Ka Saukar:
1. Mun ga gari ya yi duhu.
Mun taba shaida hakan.
An soma tsananta mana
Ba bakon abu ba ne.
Za mu yi karfin zuciya,
Babu gudu, ba tsoro.
Mun san Allahnmu, Jehobah,
Za ya kāre dukanmu.
(AMSHI)
Mu kamar tsintsiya muke,
Mai madauri daya tak.
Ba za mu ja da baya ba,
Don Jehobah yana nan,
Don Jehobah yana nan.
2. Mun yi imani da Allah,
Don shi Madaukaki ne.
Jehobah yana da iko
Kuma shi mai kauna ne.
Zai tuna da mutanensa,
Zai taimake su sosai.
Zai kunyantar da makiya,
Domin mu bayinsa ne!
(AMSHI)
Mu kamar tsintsiya muke,
Mai madauri daya tak.
Ba za mu ja da baya ba,
Don Jehobah yana nan.
3.
Mun yi tsayin dāka,
Ba ma tsoron makiya.
Mun riga mun ba da kanmu
Ga Jehobah Allahnmu.
(AMSHI)
Mu kamar tsintsiya muke,
Mai madauri daya tak.
Ba za mu ja da baya ba,
Don Jehobah yana nan,
Don Jehobah yana nan.